You are here: HomeAfricaBBC2023 12 07Article 1894541

BBC Hausa of Thursday, 7 December 2023

Source: BBC

Ko sabon taron dangin jam’iyyun adawa zai tayar da hankalin APC?

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu

A baya-bayan nan ne Jam'iyyun hamayya bakwai a Najeriya ciki har da babbar jam'iyyar hamayya ta PDP suka ɗauki matakin yin gamin-gambiza ƙarƙashin Ƙungiyar Jam'iyyun da suka damu kan abubuwan da ke faruwa wato Concerned Political Parties (CPP).

Sauran jam'iyyun da suke cikin wannan haɗaka sun haɗa da NNPP da ADC da APM da SDP da YPP da kuma ZLP.

Jam'iyyun hamayyar sun yi taron gamayyar ne karon farko a ranar Laraba inda aka yi wata ganawa tsakanin jagororin jam'iyyun bakwai a sakatariyar jam'iyyar SDP da ke Abuja, babban birnin Najeriya.

Sai dai gamin gambizar bai haɗa da Jam'iyyar Labour ba, wadda ɗan takararta ya zo na uku a babban zaɓen Najeriya na 2023.

LP ta bayyana cewa jam'iyyun da suka yi wannan taron ba su tuntuɓe ta ba.

Shugaban Jam'iyyar SDP, Shehu Musa Gabam, a jawabin da ya yi wa ƴan jarida bayan taron, ya ce matakin da suka ɗauka wani yunƙuri ne na rage ƙarfin ikon da jam'iyyar APC ke da shi a siyasar Najeriya.

Wannan yunƙuri na jam'iyyun adawa dai batu ne da al'ummar ƙasar da kuma ƴan siyasa ke ta tsokaci a kai.

Toh ko ya jam'iyya mai mulkin ta ji da wannan yunƙuri?

Hankalinmu ba zai taɓa tashi ba – APC

A martaninta, jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya ta ce ba ta damu da wannan gamin-gambiza na jam'iyyun hamayya ba, inda ta bayyana shi a matsayin 'abin kunya' wanda ba zai yi wani tasiri ba.

Daraktan yaɗa labarai na Jam'iyar APC mai mulki, Bala Ibrahim ya shaida wa BBC hakan inda ya ce matakin ihu ne bayan hari, "ai dama can da su muka yi takara muka kada su, don yanzu sun yi taron dangi, mu za mu kira shi taron abin kunya ne."

"Da can a haɗe ba su iya yin abin da zai yi tasiri ba, sai bayan sun rabu ɗaiɗaiku kuma yanzu sun zo suna neman haɗin kan su ce za su yi wani tasiri, babu wani abu da wannan zai yi." in ji shi.

A cewar sa, duk abin da ba a yi shi da safe ba, ba zai yiwu a yi shi da la'asar ba." kamar yadda ya faɗa.

'Taron dangin jam'iyyun hamayyar ya zo a makare'

Farfesa Kamilu Sani Fagge, masanin harkokin siyasa a Najeriya ya ce wannan yunƙuri na jam'iyyun hamayyar bakwai ya zo a makare kasancewar "tun lokacin da ake gwagwarmayar zaɓe, an so a samu manyan jam'iyyun da za su iya karawa da APC da PDP."

"Sai dai rarrabuwar kai ta sa suka ƙi haɗuwa." In ji masanin.

Ya bayar da misali da yadda babbar jam'iyyar hamayya ta PDP ta shiga babban zaɓen alhalin kawuna ƴaƴanta na a rabe, "Peter Obi na LP ai daga PDP yake, Rabiu Kwankwaso na NNPP ma daga PDP yake,"

"Ga gwamnoni biyar - su Wike, suma suka yi mata bore." Kamar yadda Farfesa Fagge ya bayyana.

Sai dai ya ce jam'iyyun za su iya cimma nasara idan suka haɗe suka gina jam'iyya ɗaya mai aƙida, suka kuma tsaya a bayan wani ɗan takara guda ɗaya.

A cewarsa, za su iya nasara wajen ƙalubalantar APC tare da yin nasara idan suka kashe kwaɗayinsu na son takara tare da dagewa wajen yin kamfe lungu da saƙo na ƙasar.