You are here: HomeAfricaBBC2023 05 25Article 1773905

BBC Hausa of Thursday, 25 May 2023

Source: BBC

Binciken gwamnatin Kano ya wanke Ado Doguwa daga zargin kisan kai

Alhassan Ado Doguwa Alhassan Ado Doguwa

Ma'aikatar shari'a ta jihar Kano ta bayyana cewa binciken da ta gudanar kan tuhumar da ake yi wa ɗan majalisar wakilan Tarayya, Alhassan Ado Doguwa kan laifin kisan, ya nuna cewa ba a same shi da laifin da ake zargi ba.

Lokacin da ya yi wa manema labarai bayani, kwamishinan shari'a na jihar Kano, Lawan Musa Abdullahi ya ce an samu saɓani da dama cikin bayanan da aka samu daga wurin shaidu.

Ya ƙara da cewa a yayin da suke gudanar da bincike sun gano cewa ma'aikatan asibiti ba su yi cikakken bincike kan mutanen da ake zargin an harba da bindiga ba, soboda haka ba a iya tabbatar da cewa an harbe su ba.

Kwamishinan ya bayyana cewa an gudanar da bincike kan bindigogi da harsashai da ke hannun 'yan sandan da ke tare da ɗan majalisar a lokacin da rikicin ya faru kuma babu wata shaida da ta nuna cewa an yi amfani da bindigogin, kasancewar jami'an ƴan sandan sun mayar da daidai adadin harsasan da ke a hannunsu.