You are here: HomeAfricaBBC2023 01 02Article 1689419

BBC Hausa of Monday, 2 January 2023

Source: BBC

Obasanjo ya zama tamkar ɗan baƙin ciki - Fadar Shugaban Najeriya

Shugaba Muhammadu Buhari da Tsohon Shugaban Najeriya Olusegun Obasanjo Shugaba Muhammadu Buhari da Tsohon Shugaban Najeriya Olusegun Obasanjo

Fadar Shugaban Najeriya ta mayar da kakkausan martani kan kalaman da Tsohon Shugaban Najeriya Olusegun Obasanjo ya yi a saƙonsa na sabuwar shekara.

A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Najeriya Malam Garba Shehu ya fitar, sanarwar ta ce Obasanjo ba zai taɓa daina caccakar Shugaba Muhammadu Buhari ba sakamakon Obasanjon ba zai daina baƙin ciki kan duk wani wanda ya sha gabansa a ayyukan ci gaban ƙasa ba.

Fadar shugaban ƙasar ta buga misali da cewa Shugaba Buhari ya kammala gadar Neja ta biyu bayan an yi shekara 30 ana alƙawura a kanta.

Haka kuma fadar shugaban ƙasar ta ce Obasanjo ya yi wa kudu maso gabashin Najeriya ƙarya domin ya samu ƙuri'unsu, amma Shugaba Buhari bai samu ƙuri'unsu ba amma duk da haka sai da ya yi musu aikin gadar.

Fadar shugaban ƙasar ta kuma ce Obasanjo yana baƙin ciki ne sakamakon yana ganin yadda Buhari ke samun lambobin yabo da kuma yadda shugaban ke ci gaba da da'awar cewa zai tabbatar an gudanar da sahihin zaɓe fiye da wanda ya kawo sa kan karagar mulki.

Haka kuma fadar ta zargi Obasanjo da lalata dimokraɗiyya a Najeriya bayan kitsa tsige wasu gwamnoni a ƙasar da suka haɗa da Joshua Dariye da Rashidi Ladoja da Peter Obi da Chris Ngige da Ayo Fayose.

Wannan martanin na fadar shugaban Najeriya duk na zuwa ne bayan tsohon Shugaban Najeriyar Chief Olusegun Obasanjo ya ce Peter Obi ne zaɓinsa a zaɓen 2023 haka kuma Obasanjon ya caccaki gwamnatin Shugaba Buhari.

Me masu sharhi ke cewa kan kalaman Obasanjo

Kalaman Obasanjo dai sun yi matuƙar tayar da ƙura a Najeriya inda tuni manyan jam'iyyu suka soma mayar da martani masu sharhi kuma suna tsokaci.

Dakta Abubukar Kari na jami'ar Abuja, kuma mai nazari kan harkokin siyasa a Najeriya ya ce goyon bayan da Obasanjon ke yi wa Mista Obi ba zai yi wani tasiri ga nasarar ɗan takarar ba.

Domin kuwa a cewarsa a tarihin siyasar Najeriya Mista Obasanjo ko rumfar zaɓensa bai taɓa kawowa ba.

Dakta Kari ya ce "Obasanjo dai tsohon shugaban kasa ne wanda ya mulki Najeriya har sau biyu, kuma ana iya cewa yana da karfin fada-a-ji a ciki da wajen kasar nan - ta bangare daya ke nan - to amma idan ana zaton goyon bayan da ya ba Peter Obi na iya zama hanyar samun yawan kuri'u, ana iya cewa ba shi da tasiri sosai."

Sai dai yana ganin babban tasirin goyon bayan shi ne, "zai karfafa wa magoya bayan Peter Obi gwiwa, sai dai wasu na ganin yana da tasiri a tsakanin kasashen waje a diflomasiyance, wanda Peter Obin zai iya cin gajiyar haka."