You are here: HomeAfricaBBC2022 12 07Article 1676366

BBC Hausa of Wednesday, 7 December 2022

Source: BBC

Kenya na son hadakar karbar bakuncin Gasar kofin Afirka a 2027

Hoton alama Hoton alama

Kenya na shirin hadakar karbar bakuncin Gasar Cin Kofin Afirka a 2027 tare da wata kasa daga Kudancin Afirka.

Gwamnatin Kenya ta tsara gagarumin shirin da zai kai kasar ta samu gurbin shiga Gasar Kofin Duniya a karon farko a wanda za a yi a 2030.

Tawagar da ake kira Harambe Stars ta buga Gasar Kofin Afirka karo biyu tun daga 1993, an kuma dakatar da ita shiga wasannin 2023, bayan da Fifa ta hukuntata.