You are here: HomeAfricaBBC2021 05 25Article 1269916

BBC Hausa of Tuesday, 25 May 2021

Source: BBC

Buba Marwa na shan yabo a wurin ƴan Twitter kan yaƙi da masu safarar miyagun ƙwayoyi

Shugaban Hukumar NDLEA, Birgediya Janar Mohamed Buba Marwa Shugaban Hukumar NDLEA, Birgediya Janar Mohamed Buba Marwa

Ƴan Najeriya sun karya kumallo da shugaban Hukumar da ke hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya (NDLEA) Birgediya Janar Mohamed Buba Marwa mai ritaya a kafofin sada zumunta na intanet musamman a Twitter.

Buba Marwa, wanda aka naɗa shugaban NDLEA a watan Janairun 2021, yana shan yabo daga wurin ƴan Najeriya kan yadda yake bankaɗo masu safarar miyagun ƙwayoyi a ƙasar.

A ranar Lahadi ne Hukumar NDLEA ta ce ta kama hodar ibilis da kudinta ya kai naira biliyan takwas tare da kama babban mai safarar ƙwayoyi a filin jirgin saman Legas.

Sanarwar da hukumar ta fitar ta ce an kama babban mai safarar ƙwayoyin ne da ke zama a ƙasar Brazil a ranar Juma'a 14 ga watan Mayun 2021 lokacin da yake ƙoƙarin shigo da hodar iblis a Najeriya.

Hukumar ta kuma ce ta kwace dala dubu 24,500 da aka nemi a bayar a matsayin cin hanci domin hana gudanar da bincike, matakin da ya ja hankalin ƴan Najeriya.



Tun a ranar Lahadi ƴan Najeriya ke tsokaci game da hukumar NDLEA da kuma shugabanta Janar Buba Marwa a shafin Twitter.

Sunan Buba Marwa ya kasance ɗaya daga cikin wadanda aka fi yin tsokaci a Najeriya a ranar Litinin, inda ya samu tsokaci sama da 4,000 a Twitter kawai.

Me ƴan Najeriya ke cewa?

Yawancin ƴan Najeriya na tsokaci ne kan yadda kusan kullum hukumar NDLEA ke bankaɗo masu safarar miyagun ƙwayoyi a ƙasar ƙarƙashin shugabancin Buba Marwa.

Haka kuma suna fatan ɗorewar ƙoƙarin da hukumar ke yi na ci gaba da kama masu safarar miyagun ƙwayoyi.