You are here: HomeAfricaBBC2021 05 14Article 1261540

BBC Hausa of Friday, 14 May 2021

Source: BBC

Janar Mahamat Idriss Deby: Abubuwan da Buhari shugaban Chadi suka tattauna

Buhari ya karɓi baƙuncin takwaransa na ƙasar Chadi Laftanar Janar Mahamat Idriss Deby Itno Buhari ya karɓi baƙuncin takwaransa na ƙasar Chadi Laftanar Janar Mahamat Idriss Deby Itno

A ranar Juma'a ne Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya karɓi baƙuncin takwaransa na ƙasar Chadi Laftanar Janar Mahamat Idriss Deby a Abuja, inda suka tattauna game da ci gaban ƙasashensu.

Wannan ne karon farko da Janar Mahamat mai shekara 37 ke ziyara a Najeriya tun bayan da ya gaji mahaifinsa Idris Deby Itno a matsayin shugaban gwamnatin riƙon ƙwarya ta Chadi a watan Afrilu.

A farkon watan Mayu ne Janar Mahamat ya kai irin wannan ziyara Jamhuriyar Nijar. Muhimmancin ziyarar na da girman gaske ganin yadda ƙasashen uku ke fama da hare-haren 'yan bindiga masu iƙirarin jihadi baya ga iyakoki da suka haɗa.

Dawo da dimokuraɗiyya a Chadi

Shugaba Buhari ya faɗa wa Janar Mahamat cewa Najeriya za ta tallafa wajen daidaita Chadi da kuma tabbatar da komawarta kan tsarin mulkin dimokuraɗiyya.

"Najeriya ta san irin rawar da Chadi ta taka wajen taimaka mata a yaƙi da ta'addanci kuma muna godiya sannan za mu ci gaba da wannan alaƙar", in ji Buhari.

"Nahiya da al'adu sun haɗa ƙasashenmu waje guda, saboda haka za mu taimaka a cikin duk abin da za mu iya".

Buhari ya kuma bayyana mahaifin sabon shugaban Chadin wato Idris Deby Itno a matsayin abokinsa kuma abokin Najeriya.



Tsaurara tsaro a Tafkin Chadi

Ƙasashen Chadi da Najeriya da Nijar da Kamaru na cikin hukumar kula da Tafkin Chadi mai suna Lake Chad Basin Commission (LCBC), wadda aka kafa don kula da kuma haɓaka shi.

Buhari ya tabbatar wa da takwaran nasa cewa Najeriya za ta ci gaba da ayyukanta a ƙungiyar tsaron haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen ta MNJTF.

Alaƙar Buhari da Idriss Deby

A jawabinsa, Janar Mahamat Idriss Deby ya gode wa Najeriya bisa irin goyon bayan da aka nuna musu bayan mutuwar mahaifinsa kuma tsohon shugaban Chadi.

"Kana cikin na kusa-kusa ga Marshal Itno. Na zo ne domin na ƙarfafa wannan alaƙar da kuma neman ka taimaka mana wajen shugabancinmu.

"Mun dogara a kan 'yar uwarmu Najeriya kamar yadda muka haɗa al'ada da nahiya. A shirye muke mu yi amfani da taimakonka don komawa kan tsarin dimokuraɗiyya."

Ya kuma sake nanata kudirinsa na ganin an gudanar da sahihin zaɓe nan da wata 18.