You are here: HomeAfricaBBC2021 03 29Article 1217920

BBC Hausa of Monday, 29 March 2021

Source: BBC

Kasuwar cinikin 'yan kwallo: Makomar Lukaku, Haaland, Mane, da Lingard

Dan wasan Belgium da Inter Milan Romelu Lukaku Dan wasan Belgium da Inter Milan Romelu Lukaku

Chelsea na duba yiwuwar daukar dan wasan Belgium kuma tsohon dan wasanta Romelu Lukaku, mai shekara 27, idan ta gaza daukar dan wasan Norway Erling Braut Haaland, mai shekara 20, a bazarar nan. (Telegraph)

Manchester City tana son daukar Lukaku, wanda ya zura kwallo 59 a wasanni 85 da ya murza a Inter Milan. (Calciomercato, via Manchester Evening News)

Borussia Dortmund ta sanya kudi kan Haaland ga masu son daukarsa a bazarar nan inda ta ce duk kungiyar da ke son dan wasan za ta ajiye akalla £154m. (ESPN)

Dan wasan Senegal Sadio Mane, mai shekara 28, ya bayyana cewa zai ci gaba da zama a Liverpool - koda kuwa kungiyar da Jurgen Klopp yake jagoranta ba ta samu gurbin zuwa gasar Zakarun Turai na kakar wasa mai zuwa ba. (Sun)

Kofar Manchester United a bude take ga dan wasan Ingila mai shekara 28 Jesse Lingard, wanda ke zaman aro a West Ham - kuma akwai damar sake tattaunawa domin tsawaita kwangilarsa. (Sun)

Manchester United ta tuntubi Atletico Madrid domin daukar dan wasan Sifaniya Marcos Llorente, mai shekara 26, a kan £68.5m. (AS)

Rahotanni sun ce ran shugaban Real Madrid Florentino Perez 'ya yi matukar baci' game da Manchester United saboda ta bi sawunta a yunkurin daukar dan wasan Sifaniya mai shekara 24 Pau Torres. (El Desmarque, via Mirror)

Kocin Liverpool Klopp ya sake bukatar masu kungiyar su amince a sabunta kwangilardan wasan tsakiya na kasar Netherlands Georginio Wijnaldum, mai shekara 30. (90min)

Kazalika Liverpool na gaban AC Milan da Juventus a yunkurin daukar dan wasan PSV dan kasar Netherlands Donyell Malen, mai shekara 22, a bazarar nan. (Gazetta dello Sport, via Mail)

AC Milan za ta "yi dukkan mai yiwuwa" domin daukar dan wasan Ingila mai shekara 23 Fikayo Tomori a mataki na dindindin daga Chelsea, a cewar mataimakin shugaban kungiyar Franco Baresi. (Gazzetta dello Sport, via Standard)

Dan wasan Newcastle United dan kasar Paraguay Miguel Almiron, mai shekara 27, ya ce yana 'son murza leda a kungiyoyin da ke fafatawa sosai' yayin da ake rade radi game da makomarsa a Tyneside. (Chronicle)