You are here: HomeAfricaBBC2021 03 19Article 1209160

BBC Hausa of Friday, 19 March 2021

Source: BBC

'Yan bindiga sun kashe jami'an tsaro 6 a Anambra

Jami'an tsaro akalla shida ne suka hallaka a jihar Anambra Jami'an tsaro akalla shida ne suka hallaka a jihar Anambra

Jami'an tsaro akalla shida ne suka hallaka a jihar Anambra da ke kudu maso gabashin Najeriya.

Jami'an tsaron sun hada da sojojin ruwa uku da wasu yan bindiga suka harbe a garin Awkuzu da ke karamar hukumar Oyi.

Sai kuma jami'an 'yan sanda uku da yan bindigar suka harbe a Neni da ke karamar hukumar Anaocha tare kuma da cinna wa motarsu wuta.

Al'amarin ya janyo zaman zulumi a jihar kuma ana rade radin cewa an sami wani gungun 'yan bindiga da ke kai wa jami'an tsaro hari a jihar ta Anambra.

Rahotanni sun ce yan bindigar sun harbe sojin ruwan ne da karfe biyu na rana inda suka yi awon gaba da makamansu.

Jihar Anambra na cikin jihohin da aka hallaka jamian 'yan sanda tare da kona caji ofis na yan sanda a watan Fabarerun daya gabata.