BBC Hausa of Sunday, 14 March 2021
Source: BBC
'Yan bindigar da suka sace ɗaliban makarantar aikin noma ta Jihar Kaduna sun saki wasu bidiyo, inda ɗaliban ke roƙon gwamnati ta biya kuɗin fansa domin ceto su.
'Yan bindigar sun kai hari kwalejin ce da misalin ƙrfe 11:00 na daren Alhamis kuma suka yi awon gaba da mutum 39, 23 mata da kuma maza 16.
'Yan fashin sun yi amfani ne da shafukan ɗliban wurin wallafa bidiyon a Facebook. A ɗya daga cikin bidiyon, ana iya ganin yadda suke dukan ɗliban mazansu da matansu da tsabga a wani wuri da ya yi kama da tsakiyar daji.
"Waɗannan mutanen sun kewaye mu kuma sun ce duk wanda ya yi ƙoƙarin zuwa ya cece mu za su kashe mu," in ji ɗaya daga cikin ɗliban wanda ya yi magana da harshen Ingilishi.
Ya ƙara da cewa: "Sun yi mana duka har sun ji mana raunuka sosai. Wasu daga cikinmu na kukawa kan raunkan da suka ji. Idan gwamnati ba ta zo ta cece mu da wuri ba muna cikin gagarumar matsala."
Wata mace da ta yi magana da Hausa ta bayyana cewa "mutanen nan sun faɗ mana cewa idan sojoji suka yi yunƙurin cetarmu ko ɗaya daga cikinmu babu wanda zai koma gida".
A wani bidiyon, ana iya jin ɗalibai mata da ke zaune a bayan mazan suna cewa "ku ba su kuɗin fansar kawai su sake mu don Allah" cikin Hausa da Ingilishi.
Wasu rahotanni na cewa 'yan bindigar sun buƙaci naira miliyan 500 a matsayin kuɗin fansa, kamar yadda wasu iyayen ɗliban suka shaida wa jaridar Daily Trust.
Gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufai ya sha bayyana cewa gwamnatinsa ba za ta taɓa yi wa 'yan fashin dajin afuwa ba yayin da maƙotan jihohi ke cewa sun ga amfanin sulhu da su.
Sai dai ita ma gwamnatin tarayyar ƙarƙashin Muhammadu Buhari ta tabbatar da cwea ba za ta shiga maganar sulhu da 'yan fashin ba.