You are here: HomeAfricaBBC2023 08 21Article 1829111

BBC Hausa of Monday, 21 August 2023

Source: BBC

Yau Tinubu ke rantsar da sabbin ministocinsa

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu

Babban ɗakin taro na fadar shugaban ƙasa ya fara ɗaukar harama domin rantsar da sabbin ministocin gwamnatin shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu.

A watan Afrilu ne shugaban na Najeriya ya miƙa wa Majalisar Dattijan ƙasar sunayen mutum 45 domin tantantancewa a matsayin minsitoci.

Bayan haka nan shugaban na Najeriya ya bayyana ma'aikatun da kowane minista zai riƙe gabanin ranar ta yau da ake rantsarwar.

Sai dai ko a ranar Lahadi, shugaban ya fitar da wasu sauye-sauyen da ya yi na ma'aikatu ga wasu sabbin ministocin.