You are here: HomeAfricaBBC2023 08 09Article 1821821

BBC Hausa of Wednesday, 9 August 2023

Source: BBC

Wolves ta sallami Lopetegui

Julen Lopetegui Julen Lopetegui

Kocin Wolves Julen Lopetegui ya bar kungiyar, inda tsohon kocin Bournemouth Gary O'Neil zai maye gurbinsa.

Wolves ta ce ta daɗe da fahimtar cewa Lopetegui, mai shekaru 56, yana son barin kungiyar.

Kungiyar ta kuma ce dukkan bangarorin biyu sun amince da sabanin ra'ayi kan wasu batutuwa kuma sun amince cewa kawo karshen kwantiraginsa cikin aminci shi ne mafita mafi kyau".

Wolves ta sanar da barin kocin dan Sifaniya kwanaki uku kafin a fara gasar Premier, inda za su kara da Manchester United ranar Litinin.

Kulob din ya ce "an ci gaba da tattaunawa a cikin 'yan makonnin nan, don bai wa kulob din lokacin neman wanda zai maye gurbin Lopetegui da ma'aikatansa don tabbatar da cewa 'yan wasa na cikin kyakkyawan yanayi don sabuwar kakar wasa.

Wakilin BBC Simon Stone ya fahimci cewa an rufe yarjejeniyar rabuwa tun lokacin da aka yi wasan sada zumunta da Celtic a watan jiya, amma Lopetegui ya amince ya ci gaba da ba da lokaci don nemo wanda zai maye gurbinsa.

An dauki 'yan takara da dama a matsayin wadanda za su maye gurbin Lopetegui amma O'Neil mai shekaru 40 ya burge shugabannin kuma ana sa ran za a tabbatar da shi a matsayin sabon kocin ranar Laraba.

O'Neil ya jagoranci Bournemouth a gasar Premier a kakar wasan da ta wuce, inda ta ƙare a matsayi na 15, amma an kore shi a watan Yuni kuma aka maye gurbinsa da Andoni Iraola, wanda ya jagoranci kungiyar Rayo Vallecano ta Spaniya zuwa matsayi na 11 a gasar La Liga a bara.