You are here: HomeAfricaBBC2023 02 13Article 1713524

BBC Hausa of Monday, 13 February 2023

Source: BBC

Watakila Haaland ba zai buga wasa da Arsenal ba - Guardiola

Erling Braut Haaland, dan wasan Manchester City ya ji rauni Erling Braut Haaland, dan wasan Manchester City ya ji rauni

Ranar Laraba Arsenal za ta karbi bakuncin Manchester City a kwantan wasan Premier League karawar mako na 12.

Arsenal mai maki 51 tana ta daya a kan teburi da tazarar uku tsakaninta da City ta biyu mai 48.

Sai dai watakila Erling Haaland ba zai buga wasan ba, bayan da ya ji rauni a fafatawar da City ta doke Aston Villa 3-1 a Etihad ranar Lahadi a Premier League.

Haaland wanda ya ci kwallo 25 a babbar gasar tamaula ta Ingila a bana, an sauya shi a wasan Lahadin lokacin da City ke cin 3-0.

Kociyan City Pep Guardiola ya fada cewar ''Erling ya samu buguwa, bai jin kazar-kazar.''

Kungiyar Etihad za ta koma kan teburi idan har ta doke Arsenal a Emirates ranar Laraba.

Arsenal ta ci karo da cikas a Premier, wadda Everton ta doke ta 1-0 a Goodison Park, sannan ta tashi 1-1 da Brentford ranar Asabar a Emirates.

To sai dai City ba za ta yi rashin Haaland ba koda bai buga mata wasan ba, domin bai ci kwallo ba a karawa hudu baya a waje a dukkan fafatawa.

A wasan Premier League da Tottenham ta ci City 1-0, Haaland bai buga kwallo ya nufi raga ba ko sau daya, kenan baya yin kokari sosai.

Rabon da Haaland ya ci kwallo tun ukun da ya zura a ragar Wolves ta City ta ci 3-0 ranar 22 ga watan janairun 2023.

City ta doke Arsenal 1-0 a FA Cup ranar 27 ga watan Janairun 2023 a Etihad.