BBC Hausa of Thursday, 7 December 2023
Source: BBC
Babbar jam`iyyar hamayya a Najeriya , wato PDP ta umurci`ya`yanta da suka gurfanar da ita a gaban kuliya sakamakon rigingimun cikin gida, da su janye kararrakin saboda ta samu bude hanyar sulhu da dai-daita tafiyar jam`iyyar da `ya`yan nata.
Kwamitin gudanarwar jam'iyyar ya ce, kundin tsarin mulkin jam`iyyar ya haramta wa `ya`ya kai mahaifiyarsu kara gaban kuliya.
Sanata Umar Ibrahim Tsauri wanda mamba ne a Kwamitin Amintattun na jam`iyyar PDP , ya shaida wa BBC cewa dokar dadaddiya ce amma wasu `ya`yan jam'iyyar na mata biyayya ce irin ta ganin dama:
“Ba a kai jam’iyya kara kotu, wanda duk ya kai jam’iyya kara kotu, jam’iyya ta tanadi irin hukuncin da yakamata a yi mi shi, kuma wannan shi ne dai -dai, domin yanzu mu ke bukatar jam’iyyar ta koma bisa kafafunta”
“Idan ka kai karar jam’iyya, ba ta jam’iyyar ka ke yi ba, ta kanka ka ke yi kennan, saboda haka abinda ake so shi ne duk wani abu da ya shafi laifufuka ko kuma jin ba ‘a yi ma dai- dai ba, akwai matakin da jam’iyya ta ce a bi, akwai kwamitin sassanci tun daga rumfar zabe har ya zuwa matakin uwar jam’iyyar , sai an bi wannan a zo karshe”, in ji shi.
Sai dai wasu na ganin umurnin wani sabon salo ne na kama-karya ko tirsasa wa ‘ya’yan jamiyyar PDP amma Sanata Umaru Tsauri ya nanata cewa wannan shi ne tanadin da tsarin mulki ya yi a kan wannan batu kennan:
“Ai tsarin mulki abinda ya ce kennan ayi, shi yasa aka yi mataki iri-iri idan na yi maka laifi ga wurinda za ka kai kara, ko da a irin tarukan nan da ake zabar ‘yan takara, za ka ga cewa duk kwamitin da aka tura, akan tura kwamiti guda biyu ne”, in shi
Sanata Tsauri ya ce akwai kwamitin da ake dora wa alhakin gudanar da zabe akwai kuma akwai kwamitin da za a tura ya je ya saurari kararrakin wadanda aka yi wa ba dai -dai ba a lokacin zaben.