You are here: HomeAfricaBBC2023 11 16Article 1882421

BBC Hausa of Thursday, 16 November 2023

Source: BBC

Super Eagles ta yi tuntuɓe a wasanta da Lesotho

Yan wasan Najeriya Yan wasan Najeriya

Najeriya ta fara wasannin neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya na 2026 da tuntuɓe inda ta yi kunnen doki da Lesotho 1-1.

A minti na 56 ne Lesotho ta fara jefa ƙwallo a ragar Super Eagles a wasansu na rukunin C a filin wasan Godswill Akpabio da ke Uyo, jihar Akwa Ibom ranar Alhamis.

Amma mintuna 11 bayan haka, mai tsaron baya Semi Ajayi ya farkewa Najeriya.

A ranar Lahadi ne Super Eagles za ta kara da Zimbabwe a filin wasa na Huye da ke Butare, a wasan da ya zame wa Najeriya dole ta yi nasara idan har tana son kara haskaka damarta ta samun gurbin shiga gasar cin kofin duniya na 2026.