You are here: HomeAfricaBBC2023 11 19Article 1883921

BBC Hausa of Sunday, 19 November 2023

Source: BBC

Super Eagles ta tashi 1-1 da Zimbabwe a Rwanda

Yan wasan Super Eagles Yan wasan Super Eagles

Tawagar kwallon kafa ta Najeriya ta tashi 1-1 tsakaninta da ta Rwanda ranar Lahadi a Rwanda.

Tawagogin biyu sun buga wasa na biyu-biyu a cikin rukuni na uku a wasannin neman shiga gasar Kofin Duniya da za a yi a 2026 a Amurka da Canada da Mexico.

A minti na 26 da fara wasa ne Zimbabwe ta fara cin kwallo ta hannun Walter Musona, kuma haka suka je hutu ana cin Super Eagles 1-0.

Bayan da suka koma zagaye na biyu ne Najeriya ta farke ta hannun Kelechi Iheanacho.

Wasa na biyu kenan da Najeriya ta tashi 1-1 a karawar cikin rukuni na uku, bayan da ta yi kunnen doki da Lesotho a Uyo ranar Alhamis.

Ita kanta Zimbabwe ta tashi wasan farko a cikin rukuni da Rwanda ba ci ranar Laraba.

Zimbabwe na buga wasanninta a Rwanda saboda ba ta da filin wasa mai darajar da za a buga wasannin.

Ranar 3 ga watan Yunin 2024 Super Eagles za ta karbi bakuncin Afirka ta Kudu a wasa na uku a cikin rukuni na uku.