You are here: HomeAfricaBBC2023 01 31Article 1705517

BBC Hausa of Tuesday, 31 January 2023

Source: BBC

Southampton ta kammala cinikin Sulemana

Kamaldeen Sulemana Kamaldeen Sulemana

Southampton itama ta shiga kasuwar cinikin yan wasa yan awanni kafin a kulle, inda take tattaunawa da Rennes ta Faransa, don duba yiwuwar kulla cinikin dan wasanta na gefe Kamaldeen Sulemana.

Saints sun cimma matsayar za su biya fam miliyan 22 ga dan wasan na Ghana, a kokarin da suke yi na kaucewa komawa gasar Championship ta Ingila.

Rahotanni sun nuna cewa yanzu haka ana kan gwada lafiyar dan wasan a Faransa.

Sulemana ya tafi Rennes ne daga Nordsjaelland ta Denmark a 2021, kuma kudin da Southampton za ta kashe kansa ya zarta abunda ta kashe wurin sayen Danny Ings a 2019.

Dan wasan mai shekaru 20 ya buga wa Ghana wasanni 15, da suka hada da uku a gasar kofin duniya a ta Qatar 2022.

An yi ittifakin cewa shi ne dan wasan da ya fi kowanne gudu a gasar ta kofin duniya.