You are here: HomeAfricaBBC2023 08 23Article 1830545

BBC Hausa of Wednesday, 23 August 2023

Source: BBC

Silva zai ci gaba da taka leda kaka daya a Manchester City

Bernardo Silva Bernardo Silva

Bernardo Silva ya saka hannu kan yarjejeniyar kaka daya domin ya ci gaba da taka leda a Manchester City.

Kenan kwantiraginsa zai kare a karshen kakar 2026, bayan da tun farko yarjejeniyar dan kwallon tawagar Portugal za ta karkare a 2025..

Kaka biyu baya da ta wuce an yi ta alakanta Silva, mai shekara 29 da cewar zai koma Barcelona, wasu kuma na cewar Paris St-Germain ko Al-Hilal zai koma.

Silva yana cikin 'yan wasan da suka ci wa City kofin Premier League biyar tun bayan da ya koma kungiyar a Mayun 2017.

Akwai karin bayanai........