You are here: HomeAfricaBBC2023 05 30Article 1776746

BBC Hausa of Tuesday, 30 May 2023

Source: BBC

Sai ƙarshen watan Yuni cire tallafin mai zai fara aiki - Tinubu

Shugaban Najeriya Bola Tinubu Shugaban Najeriya Bola Tinubu

Fadar Shugaban Najeriya ta fitar da wata sanarwa inda ta nemi 'yan ƙasar da su daina rige-rigen sayen man fetur, tana mai cewa sai ƙarshen watan Yuni za ta janye tallafin man.

An fitar da sanarwar ce da zimmar kawo ƙarshen zullumin da jama'a suka shiga sakamakon jawabin da Shugaba Bola Tinubu ya yi bayan rantsar da shi a ranar Litinin, inda ya ce "tallafin mai ya ƙare" ba tare da bayar da takamaiman lokacin ƙarewar tasa ba.

Jim kaɗan bayan jawabin nasa ne aka fara samun dogayen layukan motoci a gidajen sayar da man fetur a manyan biranen Najeriya.

Sai dai sanarwar ta ce jawabin na shugaban ƙasar "ba sabon abu ba ne kuma ba gwamnatinsa ce ta ɗauki matakin ba.

Kazalika ta nuna cewa an tanadi kuɗin biyan tallafin ne zuwa watan Yunin 2023 kawai.

"Kawai ya na bayyana halin da ake ciki ne, ganin cewa kasafin kuɗin gwamnatin da ta gabata game da tallafin, an tsara shi ne zuwa wata shidan farko na wannan shekarar," a cewar ofishin shugaban ƙasar.

"Hakan na nufin nan da ƙarshen watan Yuni gwamnatin tarayya ba ta da kuɗin da za ta ci gaba da biyan tallafin, abin da ke nufin ya zo ƙarshe.

"Babu buƙatar yin rige-rige wajen sayen man saboda jawabin da ya yi; ba nan take za a janye ba."

Tun farko gwamnatin Buhari ta tsara janye tallafin daga ƙarshen shekarar 2022, amma sai ta tsawaita wa'adin zuwa tsakiyar 2023 don sabuwar gwamnati ta aiwatar da shi.

Hukumomi a Najeriya sun ce tallafin mai na laƙume naira biliyan 400 duk wata a 2023.

Tuni aka fara samun dogayen layuka a gidajen mai a manyan biranen ƙasar, inda farashin litar mai ya tashi - wani wurin ya ninka har sau biyu.

Yayin jawabin nasa na ranar rantsuwa, Tinubu ya ce gwamnatinsa "za ta zuba kuɗin wajen ayyukan raya ƙasa, da ilimi, da harkokin lafiya, da kuma ayyukan da za su kyautata rayuwar miliyoyin 'yan ƙasa".