You are here: HomeAfricaBBC2024 01 12Article 1911935

BBC Hausa of Friday, 12 January 2024

Source: BBC

Pochettino na nuna damuwa kan jinyar Nkunku

Nkunku Nkunku

Kocin Chelsea Mauricio Pochettino ya ce ya damu da koma bayan da jinyar da Christopher Nkunku zai yi fama da ita.

Wasa ɗaya ɗan wasan ya buga a Chelsea a Premeir bana, tun bayan komawa ƙungiyar.

Ciwon gwiwar da ɗan wasan ya ji ya sanya shi jinyar watanni uku, kuma bai bugawa Chelsea wasa biyun da ta yi a baya ba sakamakon raunin da ya ji a kwankwaso.

"Ba dadi abin ya dame mu, muna buƙatarsa a ƙungiyar a yanzu," in ji Pochettino.

"Ana ci gaba da duba lafiyarsa, amma ba musan me yake faruwa ba ya zuwa yanzu.".

Dan wasan Faransan ya ci wa Chelsea kwallo a wasansa na Premier tilo da ya buga, suka yi nasara da ci 2-1 kan Wolves a ranar 24 ga watan Disamba, kuma kwana uku gabanin nan da shi aka fara wasan Crystal Palace.

Amma raunin da ya ji a kwankwasonsa ya sanya Nkunku bai buga wasan FA da muka ci Middlesbrough a ranar Talata.