You are here: HomeAfricaBBC2023 08 17Article 1826921

BBC Hausa of Thursday, 17 August 2023

Source: BBC

Me 'yan Najeriya ke cewa kan ma'aikatun ministocin Tinubu?

Wasu acikin sabon ministocin shugaba Tinubu Wasu acikin sabon ministocin shugaba Tinubu

Bayan shafe kimanin kwana tamanin a kan mulki, a ranar Litinin mai zuwa Shugaba Bola Tinubu zai rantsar da ministocinsa 45 da majalisar dattijan Najeriya ta tabbatar.

Wannan wata manuniya ce cewa, gwamnatin Tinubu ta gama tsayuwa, inda za ta kama aiki gadan-gadan.

Ma'aikatun da aka bai wa ministocin mafi ba-zata, akwai ta kula da babban birnin tarayya Abuja, wadda aka tura Nyesom Wike, tsohon gwamnan jihar Ribas kuma ɗan jam'iyyar adawa ta PDP. Karon farko kenan da wani mutumin kudancin Najeriya zai jagoranci ma'aikatar, aƙalla tun bayan komawar ƙasar mulkin dimokraɗiyya a 1999.

Tuni dai masharhanta da waɗanda ake mulka ke ci gaba da tsokaci a kan adadi da girman ma'aikatun da aka bai wa yankunansu a ƙasar.

Wasu masana a Najeriya dai, na ganin bisa dukkan alamu, yankin kudu maso yammacin Najeriya ne ya fi yin kane-kane da caɓawa a rabon ma'aikatun.

Suna ganin da wannan dama, sashen zai iya kankane harkokin tattalin arziki da na siyasar Najeriya.

Wani masanin kimiyyar siyasa ya shaida wa BBC cewa, wani abu da za a iya fahimta game da rabon ma'aikatun shi ne shugaban ƙasar ya fifita ɓangaren da ya fito na Kudu maso Yamma.

Sai dai, gwamnati ta musanta zargin, tana cewa bisa al'ada mataimakin shugaban ƙasa ne yake tafiyar da harkokin tattalin arziƙi a Najeriya. Kuma Shugaba Tinubu bai canza wannan al'amari ba.

Farfesa Abubakar Kari na jami’ar Abuja, ya ce muƙaman ministocin ta wani bangaren bai zo da mamaki ba, yayin da ta wani fanni yake da ban mamaki.

Ya ce, ko fizge idan aka duba, za a ga manyan ma’aikatu masu tasiri a ɓangaren tattalin arziƙi kimanin shida duk sun tafi hannun ministocin da suka fito daga yankin na Shugaba Tinubu. Ma’aikatun sun haɗar da;

  • Ma’aikatar kuɗi da tattalin arziƙi - Wale Edu


  • Ma’aikatar sadarwa da ƙirƙire-ƙirƙire da tattalin arziƙin dijital - Bosun Tuani


  • Ma’aikatar harkokin tattalin arziƙin teku - Bunmi Tunji-Ojo


  • Ma’aikatar sufuri - Adegboyega Oyetola


  • Ma’aikatar wutar lantarki - Adebayo Adelabu


  • Ma’aikatar ma’adanai - Dele Alake.


  • A cewar Farfesa Kari, waɗannan, ma’aikatu ne masu manyan hukumomi da ke da tasiri a fannin tattalin arziƙi a ƙarƙashinsu.

    Ya ce dukkan ma’aikatun, ba ma a ƙasashe masu tasowa ba, hatta ƙasashe masu ci gaban arziƙi kusan su ne manyan masu tafiyar da harkokin tattalin arziƙin ƙasa.

    Duk ɓangaren da ke da waɗannan ma’aikatu a ƙarƙashin ikonsa, in ji Farfesa Kari, to shi ke riƙe da ragamar tattalin arziƙin ƙasa, wanda kuma yake riƙe da akalar tattalin arziƙi, to shi ne zai iya sarrafa akalar siyasa.

    Martanin Gwamnatin Tarayya

    Sai dai, babban mataimaki na musamman ga shugaban Najeriya kan yaɗa labarai, Abdulaziz Abdulaziz, ya ce zargin ba gaskiya ba ne.

    A cewar, ga duk wanda ya san yadda harkar mulki take tafiya a Najeriya, ya san cewa mataimakin shugaban ƙasa ne yake gudanar da harkokin tattalin arziƙin ƙasa.

    Kuma ga majalisar kula da tattalin arziƙi ta ƙasa wadda duk gwamnonin arewa 19 ke ciki, "to da wannan ta yaya za a danne arewa?" Abdul'aziz ya tambaya.

    Ya ce akwai hukumomi da yawa masu tasiri a fannin tattalin arziƙin Najeriya da ke ƙarƙashin ‘yan arewa, inda ya bayar da misali da hukumar hana fasa-ƙwauri (kwastam).

    Jami’in ya ce, “a halin yanzu yankin arewa yana fama da muhimman matsaloli guda biyu ne, tsaro da ilimi, to idan ka duba za ka ga duk ma’aikatun waɗannan fannoni, an damƙa su ne ga ‘yan arewa.”

    Bayan rabon ma'aikatu ga ministocin, ya ce akwai kuma hukumomin tsaro na ‘yan sandan ciki wato DSS da hukumar tattara bayanan sirri ta ƙasa NIA dukkansu suna ƙarƙashin jagorancin ‘yan arewa.

    Ya ce akwai kuma buƙatar bunƙasa ayyukan gona wanda arewa ta dogara da shi, ‘’to wannan ma an bai wa mutumin arewa ne.”

    Hadimin na shugaban Najeriyar ya ce, a tsarin mulki, ba ɓangaren zartarwa ba ne kaɗai yake da iko, akwai majalisar dokoki, wadda ke tabbatar da cewa ɓangaren zartarwa, bai yi wani abu da zai tauye wani ɓangare da ma ɗaukacin ƙasar ba, inda kowa yake da wakilci.

    Sannan ya ce hatta ita kanta majalisar zartarwa ta ƙasa idan aka duba yawan mambobinta za a ga cewa ‘yan arewa sun fi yawa a cikin wannan majalisa wadda ta ƙunshi ministoci, kuma sai abin da majalisar ta amince da shi ne ɓangaren zartarwa zai aiwatar.

    Sauran Ministoci

    Wasu daga cikin ministocin da Shugaba Tinubu ya bai wa ma’aikatu sun haɗar da, tsohon gwamnan jihar Jigawa na baya-bayan nan Alhaji Muhammadu Badaru Abubakar.

    Wasu masu sharhi na ganin naɗin tsohon gwamnan a matsayin ministan tsaro ya zo da mamaki, kasancewarsa ɗan siyasa kuma fitaccen ɗan kasuwa.

    Ba a san shi da wata ƙwaƙƙwarar alaƙa ko aiki na tsaro ba.

    Sai dai, ba shi ne mutum na farko ba, wanda ba shi da tarihin aikin tsaro a baya, da aka taɓa bai wa muƙamin ministan tsaron Najeriya.

    Shi da tsohon gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle ne, wanda aka bai wa ƙaramin minista, za su jagoranci ma'aikatar tsaron Najeriya.

    A karon farko kuma, tsohon gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike ɗan jam’iyyar PDP daga kudancin Najeriya zai jagoranci babban birnin tarayyar ƙasar, Abuja.

    Ma’aikatar albarkarun man fetur ta samu Heineken Lokpobiri a matsayin ƙaramin minista, sanarwar rabon ma'aikatun dai ba ta ambaci wanda zai riƙe mukamin babban ministan man fetur ba.

    Hakan dai ya sa, wasu sun shiga raɗe-raɗin cewa tamkar magabacinsa, shi ma Tinubu mai yiwuwa shi ne zai kasance babban ministan man fetur.

    Ita kuwa ma’aikatar shari’a ta fada hannun Lateef Fagbemi.

    Wasu daga cikin sauran ministocin sun hada da:

    Ma’aiktar yada labarai da wayar da kan jama’a – Muhammad Idris

    Ministan Ilimi -Yusuf T. Sununu

    Karamin ministan gidaje da raya birane -Abdullahi T Gwarzo

    Ministan ayyukan gona da samar da abinci -Abubakar Kyari

    Ministan Ilimi – Tahir Mamman

    Ministan harkokin cikin gida -Sa’idu Alkali

    Ministan harkokin waje – Yusuf Tuggar

    Ministan lafiya – Farfesa Ali Pate

    Ministar al’adu – Barista Hannatu Musawa

    Ministan wasanni - John Enoh

    Ministan sufurin jirgin sama - Festus Keyamo

    Karamar ministar Abuja – Mairiga Mahmud

    Ministan Ilimi da fasaha - Uche Nnaji

    Ministar harkokin mata – Uju Kennedy

    Ministan ayyuka - David Umahi

    Ra'ayoyin wasu 'yan Najeriya kan naɗin

    Jama'a da dama 'yan Najeriya na ta bayyana ra'ayoyinsu, a shafukan sada zumunta da muhawara da kafafen yada labarai har da ma wuraren taruwa, game da ma'aikatun ministocin

    Ra'ayoyin dai sun bambanta yayin da wasu ke ganin wasu ministocin, an ajiye ƙwarya a gurbinta wasu kuwa na ganin cewa naɗin wasu bai dace da inda aka kai wasu ba.

    Ga wasu daga cikinsu kamar yadda muka tsakuro a shafinmu na BBC Hausa Facebook:

    Mallam Tasi'u Muhammad ya ce, "Ministocin harkokin waje da Ministan lafiya sun dace".

    Haka shi ma Uzairu Yahaya Sunkuye irin wannan ra'ayin ya bayyana a kan waɗannan ministocin biyu.

    Abubakar Abdu cewa ya yi shi kam yana kan nazarinsu kafin ya ce wani abu.

    Abdullahi Ahmed, ma cewa ya yi "ministan lafiya ya dace da ma'aikatarsa", yayin da Abdullahi Ibrahim Bulama kokura ya ce Ministan Abuja Wike ya fi dacewa da inda aka ba shi.

    Shi ma Sanusi Sani cewa ya yi wurin ma'aikatar tsaro an yi kuskure, domin a ganinsa bai dace a ba wadannan mutum biyun wadannan mukaman ba.

    Shi kuwa Mujtaba Ibrahim cewa ya yi, "Lamarin sai addu'a, domin duk ba su cancanci muƙaman da aka ba su ba..."

    A ranar Litinin 21 ga watan nan na Agusta, 2023 ake sa ran Shugaban Najeriyar Bola Ahmed Tinubu zai rantsar da sabbin ministocin a Abuja.