You are here: HomeAfricaBBC2023 08 07Article 1820225

BBC Hausa of Monday, 7 August 2023

Source: BBC

Mbappe ba zai yi atisaye da PSG ba

Kylian Mbappe Kylian Mbappe

Kylian Mbappe ba zai yi atisaye da tawagar 'yan wasan Paris St-Germain ba a lokacin da suka fara shiri a ranar Litinin na fara gasar Ligue 1.

Mbappe na takun-saka da PSG ne bayan ya ƙi yarda ya tsawaita kwantiraginsa a ƙungiyar, yayin da ake ganin ya fi son komawa Real Madrid.

Dan wasan da ya fi zira kwallo a raga a kulob din, ya ki amincewa ya tsawaita kwantiraginsa na shekara ɗaya da zai kare a bazara mai zuwa.

Don haka PSG na son sayar da shi a yanzu domin su samu kudi a kansa a maimakon barinsa ya tafi kyauta a ƙarshen kaka mai zuwa.

Sakamakon haka, aka cire Mbappe daga cikin tawagar PSG da ta yi balaguron tunkarar kakar wasa ta bana a nahiyar Asiya.

Daga baya ya ki ganawa da wakilan Al-Hilal, wadanda suka yi tayin da ya yi fice a duniya na kawo shi kungiyar ta Saudi Pro League.

PSG za ta fara kare kambunta na Faransa a gida ranar Asabar, inda za ta kara da Lorient.

Majiyoyin PSG sun ce yunkurinsu na baya-bayan nan na sasanta lamarin shi ne bai wa Mbappe tabbacin sayar da shi a kwantiraginsa na karshen kakar wasa ta bana. Amma ya yi watsi da wannan tayin.