BBC Hausa of Monday, 7 June 2021
Source: BBC
Ƙoƙarin da dakarun ƙasashen duniya ke yi na hana masu tsattsauran ra'ayi karɓe iko da wani yankin Sahel yana fuskantar mummunan ƙalubale.
Mali, inda a halin yanzu aka girke dakarun Burtaniya kimanin 400, ta fuskanci juyin mulki a karo na biyu a cikin watanni tara, abin da shugabannin yankin suka yi Allah wadai da shi.
Shugaba Emmanuel Macron ya yi barazanar janye duka dakarun Faransa su 5,100 da ke ƙasar inda jagororin juyin mulkin suka aiwatar da shawararsu ta shiga yarjejeniya da waɗannan masu iƙirarin jahadi da dakarun ke yaƙa.
A can Arewaci kuma, Sifaniya ta fice daga yaƙin ƙawancen ƙasa da ƙasa na yaƙi wanda Amurka ke jagoranta da aka yi wa laƙabi da African Lion saboda wata taƙaddama da Morocco.
Wannan ya shafi yankin Afrika ta yamma ne kawai amma zai iya yin mummunan tasiri ga sauran sassan duniya.
Wannan ɓangaren Afrika,na Sahel hanya ce ga ɗimbin ƴan cirani da ke tafiya can Arewaci zuwa Turai. Har wa yau, ita ce wata babbar kafar safarar miyagun kwayoyi da makamai da kuma masu iƙirarin jahadi.
Ƙungiyoyi masu jihadi na Islamic State da abokiyar hamayyarta ta Al-Qaeda sun ɗauki muhimmin ƙudurin mayar da hankalinsu a Afrika bayan koma-bayan da suka fuskanta a yankin Gabas ta Tsakiya.
Idan ruɗani da mummunan tsatstsauran ra'ayi da kuma rashin tsaro suka yi katutu a ƙasashe yankin Sahel kamar Mali to akwai yiwuwar ganin abubuwa guda biyu sun bijiro: na farko, wani sabon yanki da masu iƙrarin jahadi za su dinga kitsa hare hare a faɗin duniya sannan kuma na biyu, za a samu ƙaruwar ƴan cirani da ƴan gudun hijira suna mawuyaciyar tafiya zuwa can Arewaci don shiga ƙasashen Turai, saboda su tsere daga ƙasashensu.
Wannan dabarar ta yanzu za ta yi tasiri ne kawai wajen ƙoƙarin taƙaita faɗaɗar masu iƙirarin jahadin da kuma hana su mamayewa da yin iko da muhimman wurare a yankin.
Cin zarafi da jami'an tsaro ke yi
Matsalolin yankin Sahel- fari, cin hanci da rashawa,talauci rashin aikin yi da kuma rikicin ƙabilanci abin ya wuce haka. Julia Coleman, babbar mai bincike a cibiyar nazari kan ta'adanci da ke Hague ta ce galibin dabarun da suka fi raja'a a kan tsaro ba su da tasiri domin sun gaza magance manyan matsalolin da suka sa matasan ƙasar Mali su shiga ƙungiyoyi masu iƙirarin jihadi.
"A cikin shekaru takwas da suka gabata, tun da ƙasashen duniya suka kawo ɗauki a Mali in ji Ma Coleman, lamarin ya ƙara muni. Adadin ƴan ƙasar Mali da suka shiga ƙungiyoyin jihadi ya ƙaru, haka kuma yawan kai hare hare.
Wani ɓangaren wannan ta ɗaura alhakin kan take haƙƙin bil adama da jami'an tsaro ke yi da ya haɗa da kisa ba bisa shari'a ba da kuma tsare mutane bisa la'akari da ƙabilanci.
Hatta taƙaitawa da dakatar da barazana daga masu iƙirarin jahadi wata gagarumar matsala ce.
Yankin Sahel,yanki ne da ya ratsa ƙasashen Mauritania,da Mali,da Niger, da da Chad, da Burkina faso, yana da faɗi kimanin miliyan uku na da km [1.116sq miles]- inda hare haren masu iƙirarin jahadi ke yaɗuwa cikin Najeriya mai maƙwabtaka. Yankin ba shi da yawan jama'a kuma suna warwatse,galibinsu talakawa kuma babu isasshen tsaro,ga kuma kan iyakoki sakaka waɗanda masu safarar miyagun kwayoyi da mutane da kuma ƴan ta'adda ke amfani da su.
Babu ƙasa da za ta iya magance wannan ita kaɗai. Duk da dai Faransa ce ta kai ɗauki cikin gaggawa a 2013 domin hana ƙungiyoyi masu alaƙa da Al Qaeda ƙwace iko da babban birnin Mali Bamako,daga bisani an amince cewa yin ƙawance wajibi ne. Yanzu ana gudanar da aikace aikace soji guda biyu a lokaci guda.