You are here: HomeAfricaBBC2023 02 23Article 1720076

BBC Hausa of Thursday, 23 February 2023

Source: BBC

Man United ta fitar da Barca za ta ci gaba da buga Europa

Bruno Fernandez Bruno Fernandez

Manchester United ta kai gurbin 'yan 16 da za su ci gaba da Europa League, bayan da ta yi nasara a kan Barcelona ranar Alhamis a Old Trafford.

United ta yi nasarar cin kungiyar Nou Camp 2-1 a wasa na biyu a gurbin kai wa matakin 'yan 16 a gasar zakarun Turai.

Barcelona ce ta fara cin kwallo ta hannun Robert Lewandowski a minti na 18 a bugun fenariti.

Kwallo na 25 da ya ci wa Barcelona kenan a wasa 30 a dukkan karawa a bana, karo na 12 a jere da yake zura kwallo 25 ko fiye da haka a kakar tamaula.

Bayan da suka koma zagaye na biyu ne Fred ya farke, sannan Anthony ya kara na biyu.

Anthony ya canji Weghorst - United ta zura kwallo 19 daga dan wasan da ya yi canji a kakar nan a dukkan fafatawa, ba wadda ta kaita amfana da hakan a manyan gasar Turai biyar.

Manchester United wadda ta buga 2-2 a makon jiya a Nou Camp ta kai zagayen gaba da cin kwallo 4-3 gida da waje kenan.

Wasa na 15 da aka kara tsakanin kungiyoyin biyu kenan, inda United ta yi nasara a hudu da canjaras biyar Barcelona ta ci shida.

United wadda take takarar lashe kofi hudu a bana, za ta buga wasan karshe a Wembley da Newcastle United a Caraboa Cup ranar Lahadi.

Ranar Lahadi, Barcelona wadda take ta daya a teburin La Liga da tazarar maki takwas tsakaninta da Real Madrid, za ta ziyarci Almeria a wasan mako na 23.