You are here: HomeAfricaBBC2021 03 17Article 1206799

BBC Hausa of Wednesday, 17 March 2021

Source: BBC

Man City ta daura damarar lashe kofi hudu a bana

Kocin Man City Pep Guardiola Kocin Man City Pep Guardiola

Manchester City ta kai zagayen Quarter finals a Champions League karo na hudu a jere, bayan da ta doke Borussia Monchengladbach 4-0 gida da waje ranar Talata.

City ta ci kwallon farko ta hannun Kevin de Bruyne, sannan Illkay Gundogan ya kara na biyu a fafatawar da suka yi a Bucarest.

Kungiyar ta Etihad ta ci 2-0 a wasan farko da shima suka barje gumi a Puskas Arena cikin Fabrairu, sakamakon dokar hana zirga-zirga tsakanin Jamus da Burtaniya don gudun yada cutar korona.