You are here: HomeAfricaBBC2023 03 10Article 1728644

BBC Hausa of Friday, 10 March 2023

Source: BBC

Klopp ya yi mamaki da Firmino ya zabi barin Liverpool

Klopp da Firminho Klopp da Firminho

Jurgen Klopp ya ce ya yi mamaki da Roberto Firmino ya yanke shawarar barin Liverpool a karshen kakar nan.

Dan kwallon tawagar Brazil zai kawo karshen shekara takwas da ya yi a Anfield da yarjejeniyar za ta cika a karshen watan Yuni.

Liverpool ta dade tana tattaunawa da Firmino, mai shekara 31, kan tsawaita zamansa a Anfield, sai dai ya zabi barin kungiyar.

''Abin mamaki? haka ne kadan - daman ko dai zabi ci gaba da zama da mu ko kuma ya gwada sa'a a wata kungiyar - ina martaba hukuncin da ya dauka,'' in ji Klopp.

''Kuma hakan ba komai bane kan dantantakar da ke tsakaninmu da wadda Bobby yake da ita a kungiyar.''

Firmino ya ci kwallo bakwai a wasa 13 a Premier League, amma jinya ta hana shi zuwa gasar kofin duniya, wanda ya yi wata biyu bai taka leda ba.

Ya koma taka leda a wasan da Liverpool ta ci Everton cikin watan Fabrairu, amma ya koma sauyin dan wasa a kungiyar.

Yanzu Liverpool ta zabi fara wasa daga gaba da dan kwallon da ta dauka a Janairu, Cody Gakpo da take hada shi da Darwin Nunez da Mohamed Salah.

Ya shiga wasan da Liverpool ta ci Manchester United, shine ya ci kwallo na 7-0 a Anfield ranar Lahadi na 108 da ya ci wa kungiyar a karawa 354.

Firmino ya lashe Champions League da Premier League da FA Cup da EFL Cup da Club World Cup a zaman da ya yi a Liverpool.