You are here: HomeAfricaBBC2021 03 09Article 1199341

BBC Hausa of Tuesday, 9 March 2021

Source: BBC

Kano Pillars da Rangers sun raba maki a tsakaninsu

Kano Pillars da Enugu Rangers sun tashi 1-1 a gasar Firimiyar Najeriya da suka buga ranar Lahadi, karawar mako na 14.

Rangers ce ta fara cin kwallo ta hannun Ernest Governor a minti na tara da fara wasa.

Saura minti uku kungiyoyin suje hutu ne Pillars ta farke ta hannun Auwalu Malam Ali.

Tun kan wasan Pillars tana da maki 23, bayan buga karawa 13, itama Rangers maki 23 ne da ita a lokacin.

Pillars ta karasa karawar da 'yan kwallo 10 a cikin filin, bayan da aka bai wa Yusuf Maigoro jan kati.

Wasu sakamakon wasannin mako na 13 da aka buga ranar Lahadi:

Wikki 1-1 Kwara Utd

Nasarawa Utd 1-0 Lobi

Heartland 2-2 Abia Warriors

Katsina Utd 0-0 Sunshine Stars

Rivers Utd 2-0 Jigawa Golden Stars

Wasannin mako na 15 da za a buga nan gaba:


Jigawa Golden Stars da Akwa United

FC Ifeanyi Ubah da Rivers United

Mountain of Fire da Enyimba

Lobi Stars da Plateau United

Sunshine Stars da Nasarawa United

Dakkada da Katsina United

Rangers da Adamawa United

Abia Warriors da Kano Pillars

Kwara United da Heartland

Wikki Tourist da Warri Wolves