You are here: HomeAfricaBBC2021 04 29Article 1245943

BBC Hausa of Thursday, 29 April 2021

Source: BBC

Ina matukar son lashe kofuna — Harry Kane

Harry Kane dan kwallon Tottenham da tawagar Ingila Harry Kane dan kwallon Tottenham da tawagar Ingila

Harry Kane ya bayyana yadda yake son lashe kofuna a tarihinsa na sana'ar kwallon kafa.

Dan wasan ya fadi hakan ne, bayan da Manchester City ta doke Tottenham ta kuma lashe Caraboa Cup na bana na kuma hudu a jere na takwas jumulla.

Har yanzu kyaftin din tawagar Ingila mai shekara 27, bai taba lashe kofi a Tottenham ba, kuma rashin nasara a hannun City, shi ne karo na uku a wasan karshe.

Kane wanda ya fara kungiyar tun daga ta renon matasa ya ce kakar bana ba ta yi musu yadda suka bukata ba, bayan da Tottenham ke mataki na bakwai a teburin Premier.

Kwantiragin Kane zai kare a karshen kakar 2024, an yi ta alakanta shi da cewar zai bar Tottenham a karo da dama.

Kane ya ci kwallo 31 a wasa 44 da ya yi a kakar bana, wanda ya lashe kyautar gwarzon dan kwallon kafa na Premier League na shekara a makon nan da aka yi a Landan.