You are here: HomeAfricaBBC2021 04 27Article 1243537

BBC Hausa of Tuesday, 27 April 2021

Source: BBC

Iheanacho ya kusan kai Leicester gurbin Champions League

Kelechi Iheanacho na nuna murnan sa Kelechi Iheanacho na nuna murnan sa

Leicester City ta kusan samun gurbin shiga gasar Champions League ta badi, bayan da ta doke Crystal Palace 2-1 a wasan Premier da suka kara ranar Litinin.

Wilfred Zaha ne ya fara ci wa Palace kwallo a minti na 12 da take leda, bayan da ya samu tamauala daga wajen Eberechi Eze.

Sai dai Leicester ta farke ta hannun Timothy Castagne a minti na biyar da komawa zagaye na biyu, bayan da suka yi hutu.

Saura minti 10 a tashi daga karawar Kelechi Iheanaco ya zura na biyu a raga kuma na 12 da ya ci a Premier League a karawa tara.

Da wannan sakamakon Leicester ta ci gaba da zama ta uku a kan teburin Premier League da tazarar maki bakwai tsakaninta da West Ham ta biyar, kuma saura wasa biyar a karkare kakar bana.

Leicester wadda ta kai wasan karshe a FA Cup na bana a karon farko tun 1969 ta buga Champions League a 2016/17 har ta kai wasan quarter finals, bayan da ta lashe Premier a 2015/16.

Cikin wasa biyar da ke gaban Leicester nan gaba tana da mai zafi da Manchester United wadda take ta biyu a teburi da Chelsea ta hudu da kuma Tottenham ta bakwai.

Bayan da ta buga wasa 33, Leicester wadda Brendan Rodgers ke jan ragama ta kasance a mataki na uku a irin wannan matakin a kan teburi a kakar 2019-20