You are here: HomeAfricaBBC2023 03 27Article 1738784

BBC Hausa of Monday, 27 March 2023

Source: BBC

INEC ta sa ranar ƙarasa zaɓukan da ba a kammala ba

INEC chairman Mahmood Yakubu INEC chairman Mahmood Yakubu

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Najeriya INEC ta sanya Asabar 15 ga watan Afrilu a matsayin ranar ƙarasa zaɓukan da ba su kammala ba a jihohi da dama na ƙasar.

A wani saƙo da ta wallafa a shafinta na Twitter ranar Litinin, INEC ta ce ta yanke wannan shawara ce bayan wata ganawa tsakanin manyan jami'anta.

Akwai zaɓukan gwamnoni kamar a jihohin Kebbi da Adamawa, waɗanda jami'an sanar da sakamakon zaɓe suka ce ba su kammala ba a ranar 18 ga watan Maris, baya ga sauran zaɓukan 'yan majalisun dokoki, da su ma suka fuskanci irin wannan cikas.

Ɗaya daga cikin jihohi da aka samu zaɓukan da ba su kammala ba masu yawa a ranar 25 ga watan Fabrairu, ita ce Sokoto, inda ake da 'yan majalisar wakilai 11 da sanatoci 3 waɗanda duk zaɓensu bai kammalu ba.

Masu sanya ido sun soki hukumar INEC saboda matsalolin da aka samu a zaɓen shugaban ƙasa da na 'yan majalisun tarayya na ranar Asabar 25 ga watan Fabrairu, wanda Bola Ahmed Tinubu, ya yi nasarar zama sabon shugaban Najeriya.

Haka ma a ranar 18 ga watan Maris lokacin da INEC ta gudanar da zaɓen gwamnoni da na 'yan majalisar dokokin jihohi, an gamu da wasu daga cikin matsalolin da aka samu a zaɓen INEC na farko.