You are here: HomeAfricaBBC2023 06 05Article 1780613

BBC Hausa of Monday, 5 June 2023

Source: BBC

Guardiola na fatan Gundogan zai tsawaita zamansa a Man City

Pep Guardiola na fatan Ilkay Gundogan zai saka hannu kan sabuwar yarjejeniyar Pep Guardiola na fatan Ilkay Gundogan zai saka hannu kan sabuwar yarjejeniyar

Pep Guardiola na fatan Ilkay Gundogan zai saka hannu kan sabuwar yarjejeniyar ci gaba da taka leda a Manchester City.

Kwantiragin dan wasan zai kare a karshen kakar bana, wanda ya ci kwallo biyun da ya bai wa City damar lashe FA Cup ranar Asabar.

City ta yi nasarar lashe kofin bayan cin Manchester United 2-1 a Wembley, kofi na biyu da ta dauka bayan ta lashe Premier League.

City za ta buga wasan karshe a Champions League da Inter Milan, kuma watakila shi ne wasan karshe da zai buga wa kungiyar ta Etihad.

Guardiola da Gundogan sun kulla alaka mai karfi a tsakaninsu, kuma shi ne dan wasan farko da kociyan ya fara dauka a 2016.

Ke nan Gurdiola da Gundogan sun dauki kofi 11 tare, yayin da 'yan wasa suka zabi Gundogan kyaftin din kungiyar, bayan da Fernandinho ya yi ritaya a bara.

Gundogan dan kasar Jamus, ya ci kwallo biyu daga ukun da City ta ci Aston Villa a wasan karshe a bara a Premier League.

Haka kuma ya zama na farko da ya ci kwallo a ƙanƙanin lokaci a FA Cup, wadda ya fara cin Manchester United a dakika 13 da fara tamaula.