You are here: HomeAfricaBBC2021 04 19Article 1236439

BBC Hausa of Monday, 19 April 2021

Source: BBC

Gobarar tanka ta yi ajalin mutum 7 da kona gidaje 50 a Benue

Hadurra da ke haifar da fashewar tankar mai ta zama ruwan dare a Najeriya Hadurra da ke haifar da fashewar tankar mai ta zama ruwan dare a Najeriya

Aƙalla mutum bakwai ne suka hallaka a wata mummunar gobara da ta tashi sakamakon fashewar tankar mai a jihar Binuwe da ke tsakiyar Najeriya.

Wata tankar dakon mai dauke da fetur ta fadi a kan hanya a yayin da abin da ke ciki ya zube a garin Oshigbudu na jihar Binuwe.

Shaidu sun ce wutar daga tankar da ke konewa ta afkawa wasu gidaje da ke kusa da wurin da hadarin ya faru.

Babban Sakataren Hukumar ba da agajin Gaggawa ta Jihar Benuwai, Mista Emmanuel Shior ya shaida wa manema labarai a ranar Lahadi cewa, gobara ta tashi ne bayan hadarin tankar, inda ta hallaka mutane da dama tare da lalata gidaje 50.

Hadurra da ke haifar da fashewar tankar mai ta zama ruwan dare a Najeriya, ana dora alhakin hakan kan lalacewar hanyoyi.

A watan Yulin 2019, aƙalla mutane 45 suka mutu yayin da sama da 100 suka ji rauni a yanki da hadarin baya baya