You are here: HomeAfricaBBC2023 11 14Article 1880969

BBC Hausa of Tuesday, 14 November 2023

Source: BBC

Dalilin soke bizar 'yan Najeriya bayan isar su Saudiyya

Jirgin Air Peace Jirgin Air Peace

Hukumomi a Najeriya sun ce sun fara bincike kan takamaiman dalilan da suka janyo soke bizar wasu gomman ‘yan kasar bayan sun sauka a Saudiyya ranar Lahadi.

Fasinjojin 264 waɗanda akasarinsu suka fito daga Legas da Abuja, sun isa filin jirgin sama na King Abdulaziz da ke Jidda a jirgin Air Peace, amma sai Saudiyya suka soke bizarsu, kuma nan take suka nemi a mayar da su gida.

Shugaban ƙungiyar kamfanoni da ke shirya aikin Hajji da Umara a Najeriya, Yahya Suleiman, ya faɗa wa BBC cewa mutanen sun je Saudiyya ne domin halartar taron kasuwanci tsakanin Saudiyya da ƙasashen Afirka, wanda aka gudanar a makon jiya.

Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya ta ce tana so ta gano ko matsalar da aka samu ta shafi ofishin jakadanci ne, ko kuma wasu dokoki aka karya da suka shafi sufurin jiragen sama.

Ita ma ƙungiyar kamfanonin shirya aikin Hajji da Umara ta Najeriyar ta ce ta fara nata bincike kan lamarin.

Al'amarin ya faru ne jim kaɗan bayan Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gana da shugabanni da 'yan kasuwar Saudiyya, har ma da na ƙasashen Larabawa yayin taron da aka yi tsakaninsu da ƙasashen Afirka.

Har yanzu, Najeriya ba ta warware rikicin hana wasu 'yan ƙasar bizar shiga Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE) ba, duk da sanarwar da gwamnatin Tinubu ta fitar cewa UAE ɗin ta ba da umarnin cire haramcin.

'Ba Umara suka je yi ba'

Cikin wata sanarwa, Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya ta ce za ta tabbatar da cewa ta ɗauki matakan da za su kare aukuwar hakan a nan gaba.

Sai dai ba ta yi wani ƙarin haske ba kan bayanan da ta samu kawo yanzu, tana mai cewa sai ta kammala bincike.

Sai dai shugaban ƙungiyar kamfanoni da ke shirya aikin hajji da Umara a Najeriya, Yahya Suleiman, ya ce bincikensu ya nuna cewa mutanen ba aikin Umara suka je yi ba kamar yadda rahotonni suka bayyana tun da farko.

"Ba Umara suka je ba domin ba bizar Umara suka je da ita ba," in ji shi yana mai cewa, bizar 'yan yawon buɗe-ido suka je da ita domin halartar taron 'yan kasuwa da Saudiyya.

"Sun je da bizar 'yan yawon buɗe-ido ta kasuwanci ne, kuma ba ma a Najeriya ake yin ta ba. A intanet ake yi, da kuma wasu kamfanoni da aka bai wa damar a Saudiyya, waɗanda mu ba mu san su ba."

Ya ƙara da cewa an soke bizar tasu ne saboda sun isa Saudiyya a makare - bayan an kammala taron.

BBC ta yi yunƙurin tabbatar da iƙirarin nasa a Ma'aikatar Harkokin Waje ta Najeriya, amma mai magana da yawunta ya ce ba za su ce komai ba har sai sun kammala bincike.