BBC Hausa of Wednesday, 15 November 2023
Source: BBC
Masana harkokin siyasa a Najeriya sun fara tofa albarkacin bakinsu kan kalaman ɗan takarar shugaban ƙasar ƙasar a jam'iyyar PDP Atiku Abubakar, na buƙatar haɗin kan sauran jam'iyyun hamayya domin kawar da APC mai mulki.
Masana irin su Farfesa Kamilu Sani Fagge suna da ra'ayin samun haɗakar jam'iyyu masu ƙarfi ka ya zama wani tagomashi ga siyasar Najeriya.
A baya a cewar Farfesan sai da jam'iyyar da Atiku ke takara a cikinta ta PDP ta shafe shekara 16 tana mulki a ƙasar, amma ƙawancen da aka samu mai ƙarfi ya haifar da jam'iyyar APC da ta ƙalubalance ta kuma har ya zuwa yanzu ita take mulki.
To amma game da kiran da Atiku ya yi, Farfesa Fagge ya ce, "ya so ya ɗan makara saboda tuntuni kiran da ake sha'awa a ga 'yan siyasar sun fito sun yi a karan kansu amma a lokacin da aka so hakan ba ta samu ba.
"Son zuciya da buƙata irin ta raɗin kansu ta hana manyan 'yan siyasa da jam'iyyun adawa su zo su haɗa kansu waje ɗaya su yi hakan".
A fahimtar Farfesan wasu jam'iyyun ba za su amsa wannan kira na Atiku ba, ganin cewa jam'iyyun ba su suka nemi haka ba a buƙatar kansu.
Na biyu kuma ya ce zaɓe ya yi nisa yanzu, akwai kimanin shekara uku zuwa uku da rabi ta ta yi saura, don haka haƙurin dunkulewa wuri guda ka iya zama da kamar wuya a wurin jam'iyyun.
A tsarin siyasa irin ta Najeriya "akan ji ɗuriyar jam'iyyun siyasa ne kawai a lokutan zaɓe, amma bayan zaɓe ba a wani damu da tasirunsu ba.
"Kiran da ya yi wasu ba za su yarda ba, saboda a siyasar Najeriya ko wanne ɗan takara ya fi so ya yi mulki ba ya taimaka waninsa ya yi ba".
Farfesa ya ce wani abu da zai ƙara sa firgici a sauran jam'iyyun da aka nemi haɗin kansu shi ne, "yadda Atiku yake tsalle daga wannan jam'iyya zuwa waccen, sannan wadda duk yake ciki shi ke fitowa a matsayin ɗan takara" wannan zai sake haifar da rashin aminci tsakaninsu.