You are here: HomeAfricaBBC2023 03 22Article 1735895

BBC Hausa of Wednesday, 22 March 2023

Source: BBC

An ga watan azumin Ramadan a Najeriya

Watan Ramadan Watan Ramadan

Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa'ad Abubakar na uku ya sanar da ganin jaririn watan Ramadan na shekarar 2023 a wasu sassan Najeriya.

A jawabin da ya yi na sanarwar wanda aka sanya a shafin Facebook na kwamitin ganin watan, Sarkin Musulmin ya ce an ga watan ne bayan samun rahotanni daga shugabannin addinin Musulunci da ke wasu jihohin ƙasar.

Hakan na nufin ranar Alhamis 23 ga watan Maris din 2023 ne za ta kasance daya ga watan Ramadan.