You are here: HomeAfricaBBC2023 09 12Article 1843007

BBC Hausa of Tuesday, 12 September 2023

Source: BBC

Ambaliya ta hallaka sama da mutum 2000 a Libya

Ruwan ya janyo mummunar ambaliya tare da zaftarewar ƙasa da kuma lalata gidaje da tituna Ruwan ya janyo mummunar ambaliya tare da zaftarewar ƙasa da kuma lalata gidaje da tituna

Aƙalla mutum dubu biyu ne suka rasu da dama kuma suka ɓace bayan da wata mahaukaciyar guguwa mai tafe da mamakon ruwan sama ta haddasa ambaliya a yankin gabashin Libya.

Ruwan ya janyo mummunar ambaliya tare da zaftarewar ƙasa da kuma lalata gidaje da tituna da dama a yankin.

Zuwa yanzu dai rahotanni na nuna cewa wajen da wannan ambaliya ta fi yuwa barna shi ne birnin Derna mai tashar jirgin ruwa inda madatsun ruwa biyu da kuma gadoji hudu suka rushe.

Kuma galibin birnin na cikin ruwa tsundum.

An ayyana yankin a matsayin wanda mummunan bala’i ya afka wa tare da ayyana kwana uku na makoki.

Bayanai sun nuna cewa abu ne mai wuya a iya bayyana yawan mutanen da suka halaka saboda babu hanyoyin sadarwa sosai.

Sannan kuma ga rashin tartibiyar gwamnati, sakamakon yaƙin da aka kwashe wajen shekara goma ana yi tsakanin manyan abokan gaba biyu a ƙasar.

Sojojin ƙasar ta Libya bakwai ne aka bayar da rahoton sun ɓace a lokacin da suke aikin agaji.

Jami’ai a gabashin ƙasar da ke ƙarƙashin ikon gwamnatin da ƙasashen duniya ba su amince da ita ba sun ayyana dokar hana fita, yayin da suka bayar da umarnin rufe makarantu da shaguna.

Su ma biranen Misrata da Benghazi, da Sousse, da kuma Al-Marj da ke gabashin ƙasar duk lamarin ya shafe su.

Tun a ranar Lahadi ne mahaukaciyar guguwar mai tafe da ruwa da aka yi wa lakabi da Daiel ta sauka a ƙasar ta Libya.

Masana sun yi gargaɗin cewa sauyin yanayi na duniya na nufin za a samu ƙaruwar tururi a lokacin bazara, wanda hakan zai haddasa mamakon ruwa da iska.

A yanzu mahaukaciyar guguwar mai tafe da mamakon ruwan saman ta isa yammacin Masar.

Ma’aikatar harkokin wajen Turkiyya ta ce za ta tura jiragen sama uku da za su kai ma’aikatan agaji da kuma kayan taimako zuwa kasar ta Libya.

Tun shekara ta 2014 Libya ke ƙarƙashin mulkin abokan gabar biyu bayan kashe daɗaɗɗen shugaban ƙasar Muammar Gaddafi a 2011.

Gwamnatin Firaminista Fayez al-Serra wadda ke samun goyon bayan majalisar ɗinkin duniya na yaƙi da tawayen Janar Khalifa Haftar wanda ƙasashe da hukumomin duniya ba su amince da mulkinsa ba kuma yake rike da iko a yankin gabashin ƙasar.