You are here: HomeAfricaBBC2023 12 07Article 1893854

BBC Hausa of Thursday, 7 December 2023

Source: BBC

Abu biyar game da Liliana Mohammed, Baturiyar da ta sauke Kur'ani a Kano

Malama Liliana Mohammed Malama Liliana Mohammed

A farkon makon nan ne, hotunan wata dattijuwar Baturiya rike da allon saukar karatun al-Kur'ani mai zayyana, cikin shigar hijabi, suka cika shafukan sada zumunta.

Mutane sun yi ta bayyana sakonnin taya murna da fatan alheri ga Malama Liliana Mohammed saboda wannan gagarumar bajinta da ta yi a rayuwa.

Ba a dai cika samun masu yawan shekaru da ke yin saukar Al-kur'ani ba.

To ko wace ce dattijuwa Liliana Mohammed?

Ga abu biyar game da rayuwarta:

Asalinta

Ainihinta 'yar kasar Bulgaria ce, kuma aure ne ya kai ta Kano. A yanzu, Liliana Mohammed tana da shekara 62 a duniya. Kuma in ji ta, abubuwa da yawa ne ke burge ta game da mazauninta na yanzu, wato Kano.

A cewar jaridar Daily Nigerian ta intanet Baturiyar ta zo Kano ne fiye da shekara 30 da ta wuce, bayan ta auri wani dan kasuwa marigayi Ibrahim Sambo a kasar Bulgaria.

Kuma dattijuwar ta haifi 'ya'ya biyu.

Liliana Mohammed ta yi bikin saukar Kur'ani ne tare da sauran daliban makarantar Islamiyya ta Mamba’irrahman a ranar Asabar, 2 ga watan Disamba.

Ta ce yanayi a birnin Kano, na da karfafa gwiwar ayyukan ibada na addinin Musulunci, musamman idan ta kwatanta da kasar da ta fito.

"Ta fuskar lokaci. Lokutan sallah da na azumi sun dace matuka. Tsawon dare da na rana, kusan daya ne. Ba kamar wani sashen na duniya ba, inda ake da sa'a biyar kawai a lokacin dare."

Ta ce shi kansa yanayin muhalli a Kano yana da burgewa da karfafa gwiwa. A lokacin kiran sallah, duk inda mutum yake zai ji. Ta ce hakan yana da karfafa gwiwa, sannan ga mutane a ko'ina suna sallah a lokaci.

Babban abin farin ciki a rayuwa

Liliana Mohammed ta ce saukar karatun Alkur'ani, wani babban abin godiya ne da farin ciki a rayuwarta.

Ita ma 'yar autar dattijuwar, Hamida Ibrahim Sambo ta ce sun yi matukar farin ciki da wannan cikar burin rayuwa na mahaifiyarsu.

A cewarta shi ne muhimmin abin farin ciki da ya samu rayuwar danginsu.

"Hakikanin gaskiya ma shi ne abin da ya fi sanya su farin ciki a duniya. Haihuwa, aure duk ba su kawo wannan farin cikin ba, irin na Musuluncin da ta karba."

Hamida ta ce mahaifiyarta sun yi rayuwa da mahaifinsu wanda ya riga mu gidan gaskiya kimanin shekara 13 da ta wuce, ba tare da ta karbi Musulunci ba, sai da Allah ya yi masa rasuwa.

Ta yi ta maimaita kalmar godiya ga Allah. Tana cewa: "Alhamdulillahi! Ga shi yanzu tana iya daukan Kur'ani ta yi karatunta".

Labarin saukarta

Ta ce ta shiga makarantar Islamiyya ta Manba'ir Rahman kimanin shekara goma da ta wuce, bayan ta karbi addinin Musulunci.

“Na fara karatu ne a gida, saboda yawan shekaruna. Mai koyar da ni Alkur'ani, Malama Hafsa, tana zuwa gida ne ta biya mini. Mun fara ne daga farko, inda take min rubutu da haruffan boko har zuwa lokacin da na fara gane haruffan Larabci.

“Ita ce ta ci gaba da koyar da ni karatun Kur'ani da haruffan Larabci har na zo na fara iya karantawa da kaina."

Liliana ta ce daga nan, sai suka ci gaba, ana biya mata karatu aya zuwa aya, sura bayan sura har zuwa ran da ta yi sauka.

Tasirin karbar Musulunci

Malama Liliana Mohammed ta ce daya daga cikin abubuwan da take alfahari da su game da karbar addinin Musulunci a rayuwarta, shi ne samun kwanciyar hankali da nutsuwa.

Ta kara da cewa, Musulunci ya taimake ta wajen kara fahimtar abubuwa masu yawa a rayuwa.

Wani abin ban sha'awa da Liliana Mohammed ta ce ta fahimta game da Alkur'ani mai girma da ta sauke, shi ne: "Yayin da kake karanta Kur'ani mai tsarki, shi ma Kur'ani yana karanta ka. Ina jin kwanciyar hankali da nutsuwa."

Karatun Hadda

Liliana Mohammed ta ce ba a gama ilmi a rayuwa. A kullum mutum yana sa burin ya kai inda ba kai ba.

Ta ce don mutum ya gama makaranta, ba hakan yana nufin ya gama ilmi ba ne.

"Mutum yana ci gaba da koyo ne," in ji Liliana.

Ta kuma ce tana da burin ci gaba da karatu, duk da yake tana ganin kamar shekarunta sun yi nisa ta iya haddace Kur'ani, "amma abu ne mai kyau mutum ya sa niyya".

Malama Liliana ta ce bayan mutum ya yi sauka, abu ne mai kyau kuma a mayar da hankali wajen Tajwidi.