You are here: HomeAfricaBBC2021 04 12Article 1230907

BBC Hausa of Monday, 12 April 2021

Source: BBC

Isa Ali Pantami: Da gaske Amurka ta sanya ministan cikin jerin 'yan ta'adda?

Ministan sadarwa Isa Ali Pantami Ministan sadarwa Isa Ali Pantami

Rahoton da wasu jaridun Najeriya suka wayi gari da shi ranar Litinin da ke ikirarin cewa Amurka ta sanya sunan ministan sadarwa Isa Ali Pantami a cikin jerin 'yan ta'addan duniya ya ja hankalin 'yan kasar.

Kodayake jaridun da suka wallafa rahoton ba sanannu ba ne, batun ya ja hankali sosai musamman a shafin Twitter inda ya kasance daga daga cikin manyan batutuwan da aka fi tattaunwa a kai a shafin a yau Litinin.

Ratohon ya ambato wasu majiyoyin leken asirin Amurka suna cewa kafin nadinsa a matsayin minista, Isa Ali Pantami yana da tsattsauran ra'ayin a game da Amurka sannan yana mubaya'a da kungiyar Al-Qaeda.

Kazalika sun ambato wasu bayanai daga abin da suka kira majiyoyin leken asiri na Yammacin Duniya na cewa ministan ya yi alaka ta kut-da-kut da Mohammed Yusuf, shugaban kungiyar Boko Haram na farko kuma yana da dangantaka da Abu Qatada al-Filistini da kuma wasu shugabannin kungiyar Al-Qaeda da suka ce yana matukar girmamawa.

Jaridar Daily Independent, wadda ita ta soma wallafa wannan labari, ta yi ikirarin cewa Minista Pantami a baya yana yaba wa Abu Musab Al-Zarqawi a matsayin babban shugaba, wanda ya shiga kungiyar Al-Qaeda bayan ya yi hijira zuwa Afghanistan bayan harin da aka kai a Amurka na ranar 11 ga watan Satumbar 2001.

Sai dai babu wata kafa mai zaman kanta da ta tabbatar da wadannan bayannan da wannan jaridar ta wallafa.

'Ana neman ɓata sunan Pantami'

Jaridun da suka wallafa wannan labari ba su fito fili sun bayyana majiyoyinsu ba lamarin da ya sa wasu ke kallon labarin a matsayin shafi-faɗi.

Binciken da BBC ta gudanar ya nuna cewa babu wata hukumar tsaron Amurka da ta sanya sunan ministan a cikin jerin 'yan ta'adda na duniya.

Misali, a cikin jerin 'yan ta'adda da hukumar leken asirin Amurka ta FBI ke nema ruwa ajallo, wanda ta wallafa a shafinta na intanet, babu minista Pantami.

Ita ma hukumar tsaron Amurka ba ta sanya sunansa a cikin wadanda ke daukar nauyin ta'addanci ko ma 'yan ta'adda ba.

Mai magana da yawun Ministan, Misis Uwa Suleiman, ta shaida wa BBC Hausa cewa an buga labarin ne da zummar ɓata sunan ministan.

Ta ce wasu mutane ne da suka rasa yadda za su ɓullowa Pantami domin su muzanta shi - shi ne suka fake da ƙirƙirar labarin.

Isa Ali Pantami, malamin addinin Musulunci ne da ya yi karatunta a kasashe da dama ciki har da Saudiyya.

Tun bayan ɓullar Boko Haram, Pantami yake bayyana ƙyamarsa game da yadda take gudanar da ayyukanta, lamarin da ya sa ya taɓa yin muƙabala da shugaban ƙungiyar na farko Muhammad Yusuf inda ya ƙalubalance shi kan koyarwar ƙungiyar.

A don haka binciken BBC Hausa na yanuna cewa labarin da wasu jaridun Najeriya suka wallafa na alakanta Isa Ali Pantami da kungiyar Boko Haram ko kuma hukumomi a Amurka na nemansa bisa alaka da ta'addanci ba gaskiya bane.