You are here: HomeAfricaBBC2021 05 11Article 1257961

BBC Hausa of Tuesday, 11 May 2021

Source: BBC

Ibrahim Gambari: 'Yan fashi 'sun yi yunkurin fasa gidan shugaban ma'aikatan fadar Buhari

Ibrahim Gambari, shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa Ibrahim Gambari, shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa

Fadar shugaban Najeriya ta tabatar da abin da ta kira yunkurin da wasu suka yi na fasa gidan shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa ranar Litinin.

A wata sanarwa da Malam Garba Shehu, mai magana da yawun Shugaba Muhammadu Buhari ya wallafa a shafinsa na Tuwita ya ce wasu sun yi yunkurin fasa gidan Mr Gambari da misalin karfe uku na dare.



Gidan nasa yana kusa da fadar shugaban kasa, a cewar sanarwar.

Sai dai Garba Shehu ya ce yunkurin nasu "bai yi nasara ba."

"A kan wannan batu, 'yan sanda suna neman wanda ya yi yunkurin fasa gidan wani mai suna Maikano Abdullahi ba tare da nasara ba ranar Alhamis ta makon jiya.

"Maikano yana zaune a kan titi daya da Shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa, kusa da fadar Villa," a cewar Garba Shehu.